![]() |
Lafiya Jari ceAuthor: RFI Hausa Language: ha Genres: Science Contact email: Get it Feed URL: Get it iTunes ID: Get it |
Listen Now...
Najeriya ta ƙaddamar da dokar ta ɓaci a harkar kiwon lafiya
Monday, 2 February, 2026
A wannan makon shirin zai yi dubi ne kan dokar ta baci a harkan lafiya da gwamnatin Najeriya ta kaddamar inda ta sanar da karuwar cutuka masu alaka da gurbatacciyar iskar da jama’ar ƙasar ke shaka. Hukumar duba gari ta Najeriya ko kuma Environmental Health Council a Turance ita ta sanar da wannan dokar ta baci inda tace munin cutukan dake alaka da numfashi da kuma cutar kansa dake karuwa yasa dole gwamnati da dauki tsauraran matakan, kamar yadda shugaban hukumar Dr Yakubu Muhammad Baba ke cewa. Gurbacewar iska a muhallin ɗan adam kan faru ta hanyoyi da dama kama daga yawaitar hayaƙin da motoci ke fitarwa da kone-konen dazuka ko ƙona itace a gidajen jama’a dama masana’antu da kan fitar da tiriri mai guba, wanda kuma kai tsaye ke cutar da lafiyar ɗan adam tare da haddasa cutuka ko ta’azzarar lalura masu fama da cutukan lumfashi, lamarin da ƙwararren likita Dr Lawal Musa Tahir ke cewa illar gurɓatacciyar iska ta wuce duk inda ake tunani. Ku latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin tare da Azima Bashir Aminu........









